Wednesday 19 February 2014

Boko Haram: Mutane 40,000 sun tsallaka Niger


Hukumar dake kula da 'yan gudun hijira ta Majalisar Dinkin Duniya UNHCR ta ce kawo yanzu mutane 40,000 ne su ka gujewa rikicin Boko Haram a Nigeria su ka tsallaka zuwa makwabciyar kasar Niger.
Jami'in hukumar a Jamhuriyar Niger wanda ya bayyanawa BBC hakan, ya ce za su tallafawa dubban 'yan gudun hijirar musamman wanda ke zaune a yankin Diffa.

No comments: